Alhamis 11 Yuni 2026 - 14:37
Mashigar Hormuz Ita Ce Muhimmiyar Kofar Tattalin Arzikin Duniya

Hauza/ Shugaban Cibiyar Nazarin Manufofin Harkokin Waje, Dakta Manouchehr Muhammadi, ya ce rikici da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba yau ya fara ba, sai dai tun daga farkon nasarar juyin juya halin Musulunci aka fara wannan gaba daga ɓangaren da ya kira rundunar girman kai ta duniya.

A tattaunawarsa da Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Muhammadi ya bayyana cewa “Yaƙin Ramadan” ba wani lamari ne na daban ba a tarihin juyin juya halin Musulunci na Iran, illa dai ci gaba ne na tsohuwar gaba da adawa da aka dade ana yi wa Jamhuriyar Musulunci.

Ya ce juyin juya halin Musulunci ba kawai juyin juya hali na ƙasa ba ne, domin tun farko ya zo da taken “’Yanci, walwala, Jamhuriyar Musulunci” da kuma “Ba Gabas ba, ba Yamma ba, Jamhuriyar Musulunci”. A cewarsa, manufarsa ta wuce kifar da Shah kawai, domin babban burinsa shi ne yaƙi da masu danniya da kuma kare raunana a duniya, tare da tafiya zuwa gina tsarin Musulunci a duniya.

Muhammadi ya ƙara da cewa tun daga wancan lokaci, manyan ƙasashe musamman Amurka da tsohuwar Tarayyar Soviet suka ji tsoron wannan juyin juya hali. A cewarsa, har jami’an Soviet a lokacin sun bayyana juyin juya halin Iran a matsayin babbar barazana, saboda suna ganin zai iya yin tasiri a kan Musulman da ke cikin ƙasarsu.

Ya ce tun daga farkon nasarar juyin juya hali, maƙiyan Iran sun gina dangantakarsu da Jamhuriyar Musulunci ne bisa tunanin cewa idan su za su ci gaba da wanzuwa, to dole ne Iran ba ta wanzu ba. Saboda haka, a cewarsa, sun shirya tare da aiwatar da makirce-makirce iri-iri, ciki har da yunƙurin juyin mulki, yaƙin da aka kakaba wa Iran, rikice-rikicen cikin gida da tayar da fitintinu na ƙabilanci, amma duk sun gaza.

Muhammadi, wanda kuma mamba ne a majalisar kimiyya ta sashen ilimin siyasa na Cibiyar Imam Khumaini, ya ce dalilin gazawar waɗannan shirye-shirye shi ne juyin juya halin Musulunci ba na abin duniya kawai ba ne, illa dai juyin juya hali ne na Allah da ruhaniya.

Da yake magana kan yaƙe-yaƙen tilas na kwanaki 12 da kuma na Ramadan, ya ce an tsara “Yaƙin Ramadan” ne da wani shiri na tsawon shekaru 20, inda Isra’ila da Amurka suka cim ma matsaya cewa idan suka haɗa kisan gilla, tayar da tarzoma da yaƙin makami a lokaci guda, za su iya rusa tsarin Jamhuriyar Musulunci.

Ya ce a cikin yaƙin kwanaki 12, an fara da kashe manyan kwamandoji, sannan aka kai harin soja, sannan kuma tare da goyon bayan Amurka aka yi ƙoƙarin tada bore, amma wannan shiri bai yi nasara ba. Bayan haka ne, a cewarsa, maƙiya suka yi hasashen cewa idan suka kai hari a lokaci guda ta hanyoyi daban-daban, tsarin zai rushe cikin kwanaki biyu ko uku.

Muhammadi ya ce maƙiya sun dogara ne da bayanan leƙen asiri da suke da su a cikin ƙasar, suna tunanin cewa idan suka kai hari kan kwamandoji da cibiyoyin jagoranci, za su kassara tsarin. Amma, a cewarsa, sun yi kuskure a manyan batutuwa biyu.

Na farko, ya ce sun ɗauka tsarin Jamhuriyar Musulunci da dakarunta sun ta’allaka ne da mutum ɗaya ko wasu tsirarun mutane, alhali tsarin yana da gini da shiri tun tuni.

Na biyu kuwa, in ji shi, su ne jama’a. Ya bayyana cewa maƙiyan sun yi zaton mutane za su tsorata su kulle kansu a gidajensu, amma maimakon haka sai suka fito suka shiga fili, suka takura wa masu tayar da tarzoma, ‘yan adawa da kuma ‘yan leƙen asiri.

Shugaban cibiyar nazarin ya ƙara da cewa a yaƙin kwanaki 12, Iran ta mayar da martani ne bayan sa’o’i 10, amma a wannan sabon mataki, sa’o’i biyu kacal bayan kashe manyan jami’an soja aka mayar da martani mai ƙarfi. A cewarsa, hakan ya nuna kuskuren lissafin maƙiya ne ya juya lamarin ya zama a kansu.

Game da taƙaddama tsakanin Iran da Amurka, Muhammadi ya ce Jamhuriyar Musulunci ta fuskanci wata babbar ƙasa mai ƙarfi kamar Amurka, amma saɓanin yadda a baya tunkarar jiragen ruwan yakin Amurka kaɗai ke jefa ƙasashe cikin tsoro, wannan karon jiragen ruwan yakin Amurka sun zo kusa da gaɓar Iran sannan suka ja da baya. Ya ce wannan ya ba su mamaki, domin sun kasa fahimtar dalilin da ya sa Iraniyawa ba sa tsoron wannan ƙarfi.

Muhammadi ya jaddada cewa tun farkon juyin juya hali har zuwa yanzu, maƙiyan Iran sun kasa fahimtar abu guda, wato cewa wannan juyin juya hali na Allah ne. A cewarsa, nufin Allah ya kasance kan cin nasarar wannan juyin juya hali, kuma wannan ne ya sa maƙiyan suke ci gaba da shiga ruɗani wajen fuskantar Jamhuriyar Musulunci.

Ya ƙara da cewa daga ƙarshe, bayan kwanaki 36, su kansu maƙiyan ne suka nemi a tsagaita wuta, kuma Iran ta fito daga wannan yaƙi da ƙarfi fiye da da. Ya ce ya daɗe yana bayyana wannan ra’ayi tun shekaru da suka gabata a cikin littafinsa mai taken “Iran, wata babbar ƙasa ta musamman”, kuma a yau mutane da dama a Iran da ma duniya sun fara fahimtar hakan.

Sai dai ya bayyana cewa idan aka ce Iran babbar ƙasa ce mai ƙarfi, ba yana nufin babu wasu ƙasashe masu ƙarfi a duniya ba. A maimakon haka, ya ce Iran tana da wani irin ƙarfi na musamman, saboda tushen ƙarfinta ya bambanta da na sauran ƙasashe, domin ƙarfinta yana dogara ne da taimakon Allah.

Da yake magana kan taimakon Allah a lokuta daban-daban, Muhammadi ya ce an ga irin wannan taimako a tsoffin makirce-makircen da aka shirya wa Iran, da kuma a wannan yaƙi. Ya kuma kwatanta hakan da abin da ya faru a Tabas, inda a cewarsa aka ga irin waɗannan alamu.

A ƙarshe, ya ce kalaman Shahidin jagoran juyin juya hali cewa Iran ta kusa kaiwa ƙololuwa a baya wasu ba su yarda da su ba, amma wannan yaƙi ya nuna cewa ƙasar ta kusa isa bakin wannan ƙololuwa, saura mataki ɗaya kawai.

Muhammadi ya kammala da cewa kasancewar Iran na rike da Mashigar Hormuz, wadda ya kira muhimmiyar ƙofar tattalin arzikin duniya, ya kara nuna muhimmancin ƙasar fiye da da. A cewarsa, wannan ne ya sa ƙasashe da dama ke kallon Jamhuriyar Musulunci da mutunci da bambanci fiye da yadda suke yi kafin wannan yaƙin na Ramadan.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha